IQNA

Babban malamin Addini Na Kasar Bahrain Ya Isa Kasar Iraki

23:50 - December 26, 2018
Lambar Labari: 3483254
Babban malamin addinin musl;ucni an kasar Bahrain Ayatollah Sheikh Isa Qasem ya isa birnin Najaf na kasar Iraki daga birnin London na kasar Birtaniya.

Kamfanin dilalncin labaran iqna, Tashar talabijin ta Russia Today ta bayar da rahoton cewa, a  yau Babban malamin addinin musl;ucni an kasar Bahrain Ayatollah Sheikh Isa Qasem ya isa birnin Najaf na kasar Iraki domin gudanar da ziyarar a wurare masu tsarki na birnin na ma wasu biranen na daban.

Ayatollah Isa Qasem ya isa birnin na Najaf daga birnin London na kasar Birtaniya inda yake karbar magani a asibiti, sakamakon rashin lafiya da yake faa da ita.

Tawagar da ke tare da shehin malamain ta sanar da cewa, wannan ziyara ba ta da wata alaka da gwamnatin Iraki, manyan malaman addini na kasar Iraki ne suka gayyace shi domin ya kawo ziyara, shi ne ya karba goron gayyatarsu.

Bayanin ya kara da cewa, byan ammala ziyara  abirnin Najaf da kuma ganawac da manyan malaman addini da ke birnin, Ayatollah Isa Qasem zai nufi birnin Karbala, domin yin ziyara a hubbaren Imam Hussain (AS) da ke birnin na Karbala.

3775988

 

 

 

captcha