IQNA

Majalisar Malamai Musulmi ta Masar: Daesh Ta Kara Jawo Yaduwar Kyamar Musulunci A Duniya

20:38 - February 04, 2022
Lambar Labari: 3486904
Tehran (IQNA) Babban daraktan majalisar malaman musulmin kasar Masar a wurin baje kolin littafai na birnin Alkahira ya jaddada cewa kungiyar Daesh na kara jawo kyamar musulunci a duniya.

Shafin labarai na Al-akhbar ya bayar da rahoton cewa, Majalisar malaman musulmi ta gudanar da taro kan ta'addanci da kyamar Musulunci a wurin baje kolin littafai na birnin Alkahira a jiya Alhamis 5 ga watan Fabrairu.

Babban daraktan majalisar Samir Boudinar ya kara da cewa: "Turai na tsoron musulmi 'yan ci-rani, kuma hakan ya faru ne saboda wasu matasa sun shiga kungiyar ta'addanci ta ISIL, kuma ISIL ta  yi ikirarin cewa nahiyar Turai na da al'ummomi kafirai," in ji Samir Boudinar, babban daraktan majalisar, yana mai jaddada muhimmancin daukar hanyoyin kawo karshen kyamar Musulunci da ta'addanci, da hakan ya hada da saita tunanin wadannan musulmi masu gurbatacciyar fahimta.

Ya kara da cewa: Kungiyar ta'adda ta Daesh da tunani da akuma akidar wannan kungiya sun haifar da nuna wariya ga musulmi, da ma rarrabuwar kawuna ga musulmin bakin haure a kasashen turai, saboda wadannan musulmin ba 'yan asalin Turai ba ne.

Akidar Daesh dai ta samu asalinta ne daga akidar wahabiyanci mai tsanani da ke kafirta dukkanin musulmi matykar dai ba su shiga cikin kungiyar ba.

 

 

 

https://iqna.ir/fa/news/4033678

Abubuwan Da Ya Shafa: wahabiyanci daesh kafirta musulmi
captcha